KD PRESS ✍️
Hussaini Hussaini
Sheikh Zakzaky (H), dattijon malami ne da tun a matakin samartakarsa Allah Ta'ala ya yi masa baiwa ta musamman, ilimi, hikima, hankali da basira. Hatta a cikin sa’anninsa babu wanda ya kai shi.
Malamin da ya zarce dubban malamai ba kawai a Najeriya ba, har ma a faɗin Afrika. Maƙiyansa ma suna da tabbacin cewa shi mutum ne mai gaskiya da nagarta. Har ma Sheikh Bashir Alfurƙan ya shaida cewa, tun suna a jami’a Sheikh Zakzaky (H) ke koyar da su iziya (explanation) a cikin tsantsar ilimi.
Sheikh Zakzaky (H) ya bambanta da sauran malamai, ba wai kawai a Najeriya ba, har ma a duniya. Wannan ya nuna cewa Allah Ta'ala ya zaɓe shi a matsayin abin koyi ga al’umma.
Na koyi darussa da dama daga Sheikh Zakzaky (H). Abin da ya fi jan hankalina shi ne, yadda yake da courage wajen tsayawa a kan gaskiya duk da matsin lambar maƙiya. Haka kuma yana da unique style of leadership wanda yake ratsa zukatan mutane, musamman matasa.
Duk wanda yake son fahimtar ma’anar gaskiya da jajircewa a rayuwa, to ya duba rayuwar Sheikh Zakzaky (H).
#ZakzakySymbolOfPeace
0 Comments